Majalisar Dokokin Jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige Gwamna Siminalayi Fubara da Mataimakiyarsa, Ngozi Odu, daga mukamansu, bayan tsoma bakin Shugaban Kasa, Bola Tinubu.
Majalisar ta ɗauki matakin ne a ranar Alhamis, a yayin zaman da ta ci gaba da yi a birnin Port Harcourt, babban birnin jihar.
Tun daga farkon wannan shekara ne wasu ‘yan majalisar suka fara magana kan yiwuwar tsige gwamnan, sakamakon zarge-zarge da suka shafi yadda ake tafiyar da wasu ayyukan gwamnati, tare da rikice-rikicen siyasa da suka dabaibaye jihar.
Sai dai tsoma bakin Shugaban Kasa ya kawo sassauci, lamarin da ya sa majalisar ta dakatar da shirin tsige gwamnan da mataimakiyarsa a halin yanzu.
Majalisar Rivers Ta Dakatar Da Shirin Tsige Gwamna Fubara Bayan Sa-Bakan Tinubu

