Majalisar Rivers Ta Dakatar Da Shirin Tsige Gwamna Fubara Bayan Sa-Bakan Tinubu

Majalisar Dokokin Jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige Gwamna Siminalayi Fubara da Mataimakiyarsa, Ngozi Odu, daga mukamansu, bayan tsoma bakin Shugaban Kasa, Bola Tinubu.

Majalisar ta ɗauki matakin ne a ranar Alhamis, a yayin zaman da ta ci gaba da yi a birnin Port Harcourt, babban birnin jihar.

Tun daga farkon wannan shekara ne wasu ‘yan majalisar suka fara magana kan yiwuwar tsige gwamnan, sakamakon zarge-zarge da suka shafi yadda ake tafiyar da wasu ayyukan gwamnati, tare da rikice-rikicen siyasa da suka dabaibaye jihar.

Sai dai tsoma bakin Shugaban Kasa ya kawo sassauci, lamarin da ya sa majalisar ta dakatar da shirin tsige gwamnan da mataimakiyarsa a halin yanzu.

More from this stream

Recomended