Majalisar dokokin jihar Kano ta tabbatar da Gawuna a matsayin mataimakin gwamna

Majalisar dokokin jihar Kano, ta tabbatar da Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin sabon mataimakin gwamnan jihar.

Gawuna ya maye gurbin Farfesa Hafiz Abubakar wanda ya yi murabus ranar biyar ga watan Agusta.

Majalisar ta tabbatar da nadin a wani zama da shugabanta Kabiru Alahsan Rurum ya jagoranta inda shugaban masu rinjaye na majalisar, Baffa Babba Dan-agundi ya gabatar da kudirin tantance Gawuna.

Kudirin ya samu goyon bayan, Zubairu Masu,wakilin karamar hukumar Sumaila a majalisar,bayan amincewa da kudirin da gagarumin rinjaye daganan an nemi mutumin da za a tantance da ya bayyana nasarar da ya samu a muƙamin da ya rike na kwamishinan aiyukan noma.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya,ya rawaito cewa a ranar Litinin ne gwamna, Ganduje ya mika sunansa ga majalisar domin tantancewa da kuma tabbatar da shi a matsayin mataimakin gwamna.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...