Majalisar dokokin jihar Kano, ta tabbatar da Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin sabon mataimakin gwamnan jihar.
Gawuna ya maye gurbin Farfesa Hafiz Abubakar wanda ya yi murabus ranar biyar ga watan Agusta.
Majalisar ta tabbatar da nadin a wani zama da shugabanta Kabiru Alahsan Rurum ya jagoranta inda shugaban masu rinjaye na majalisar, Baffa Babba Dan-agundi ya gabatar da kudirin tantance Gawuna.
Kudirin ya samu goyon bayan, Zubairu Masu,wakilin karamar hukumar Sumaila a majalisar,bayan amincewa da kudirin da gagarumin rinjaye daganan an nemi mutumin da za a tantance da ya bayyana nasarar da ya samu a muƙamin da ya rike na kwamishinan aiyukan noma.
Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya,ya rawaito cewa a ranar Litinin ne gwamna, Ganduje ya mika sunansa ga majalisar domin tantancewa da kuma tabbatar da shi a matsayin mataimakin gwamna.