
Shugaban majalisar dokokin jihar Kano, Jibril Isma’il Falgore ya jagoranci rantsar da sababbin yan majalisar dokokin jihar su biyu.
Sababbin yan majalisar da aka rantsar sun hada da Sa’ad Aminu Saad dake wakiltar al’ummar karamar hukumar Ungoggo da kuma Nabil Sarki Aliyu Daneji dake wakiltar al’ummar karamar hukumar Kano Municipal.
Dukkanin yan majalisar sun samu nasara ne a zaɓen cike gurbi da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa INEC ta gudanar biyo bayan gurbi da aka samu a mazaɓunsu.
Dukkaninsu sun lashe zaben ne a ƙarƙashin jam’iyar APC kuma sun maye gurbin iyayensu ne da suka rasu a rana ɗaya.
Bayan kama rantsuwar aikin yan majalisun biyu sun ci alwashin yin aiki tukuru tare da sauke nauyin da al’ummar su suka ɗora musu.

