Majalisar dokokin Jigawa ta dakatar da shugabannnin ƙananan hukumomi uku

Majalisar dokokin jihar Jigawa ta dakatar da wasu shugabannin ƙananan hukumomi uku kan zargin yin tafiya kasar waje ba tare da izinin majalisar dokokin jihar ba da na bangaren zartarwa.

Shugabannin da aka dakatar sun haɗa da Mubarak Ahmad na ƙaramar hukumar Birniwa sai Rufa’i Sanusi na Gumel da kuma Umar Baffa na ƙaramar hukumar Ƴankwashi.

Ana zargin shugabanni uku ne da tafiya kasar Rwanda ba tare da izini ba.

Majalisar ta ɗauki matakin ne bayan da shugaban kwamitin ƙananan hukumomi, Aminu Zakari Tsubut ya gabatar da kudirin dakatar da shugabannnin.

Ya ce gabanin tafiyarsu majalisar ta bayar da umarni ga shugabannin ƙananan hukumomi da kada su yi tafiya ko ina saboda shirye-shiryen kasafin kuɗin shekarar 2024 da kuma gabatar da shi gaban majalisar da gwamna zai yi.

Har ila yau majalisar ta kafa kwamiti karkashin shugaban masu rinjaye na majalisar, Lawan Muhammad Dansure da ya gudanar da bincike kan lamarin kana ya miƙa rahoto cikin makonni huɗu.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...