Majalisar Dattawan Najeriya ta kawo dokar da za ta sa gwamnoni da ciyamomi su bi dokar Kotun Koli kan ƴancin ƙananan hukumomi

Daga Sabiu Abdullahi

Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da kudirin da ke tilasta wa gwamnonin jihohi da shugabannin kananan hukumomi su bi hukuncin Kotun Koli game da asusun kananan hukumomi.

Wannan hukunci ya tanadi cewa kudaden da aka ware wa kananan hukumomi su kasance kai tsaye don amfani da su wajen ayyukan da aka kebe musu, wanda zai taimaka wajen inganta rayuwar ‘yan Najeriya.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godwin Akpabio, ya bayyana muhimmancin wannan kudiri a kasa baki daya.

Ya ce, “Mun yarda da cewa Kotun Koli ita ce babbar kotun kasar nan, kuma ba za ta yanke hukunci ba tare da an tabbatar da aiwatar da shi ba.”

Kudirin, wanda Sanata Tony Okechukwu Nwoye ya dauki nauyi, yana nufin dakatar da gwamnatocin jihohi daga kafa dokokin da ke tauye ‘yancin kananan hukumomi, kamar yadda Sashe na 7 na Kundin Tsarin Mulki ya tanada.

More News

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...

Sojojin Najeriya Sun Musanta Jita-jitar Mutuwar Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja

Daga Sabiu AbdullahiRundunar Sojojin Najeriya ta karyata rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja,...