
A ranar Laraba ne majalissar dattawa ta tabbatar da Taiwo Oyedele a matsayin karamin ministan a ma’aikatar kuɗi.
Majalisar ta tabbatar da shi ne biyo bayan tantacewar da ta yi masa inda ya amsa tambayoyi a gabanta.
A makon da ya gabata ne shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya mikawa majalisar sunan Oyedele domin ta sahale masa ya naɗa shi a matsayin minista kuma mamba a majalisar zartarwa ta tarayya .
Kafin a naɗa shi muƙamin ministan Oyedele shi ne shugaban kwamitin shugaban kasa kan batun haraji.
Oyedele zai maye gurbin tsohuwar ministar ma’aikatar, Doris Uzoka Anite.

