Magoya bayan Ambode sun gudanar da zanga-zangar lumana

Magoya bayan gwamnan jihar Lagos, Akinwumi Ambode sun gudanar da wata zanga-zangar lumana domin nuna goyonsu kan takarar gwamnan a karo na biyu.

Masu zanga-zanga sun dage kan cewa dole ne jam’iyar APC ta bawa kowanne dan takara dama a zaben fidda gwanin gwamnan da za a gudanar ranar Litinin.

Magoya bayan gwamnan sun yi jerin gwano tun daga Maryland ya zuwa Freedom Park dake Ojota.

Takarar gwamna Ambode a karo na biyu na fuskantar adawa daga wasu masu ruwa da tsaki a jam’iyar da suke zargin gwamnan ya yi watsi da su.

Tsohon gwamnan jihar Lagos kuma jagoran jam’iyar APC na kasa, Bola Ahmad Tinubu na daga cikin na gaba-gaba wajen nuna adawa da takarar gwamnan.

More News

Atiku ya bayar da tallafin miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya bayar da gudunmawar naira miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri babban birnin...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

Mutanen Sokoto na ta murnar kashe ƙasurgumin ɗanbindigar nan Halilu Buzu

Mazauna yankin Sokoto da kewaye na murnar kashe wani kasurgumin shugaban ‘yan bindiga, Kachallah Halilu Buzu, da sojojin Najeriya suka yi a farmakin da...