Ma’aikatan ƙananan hukumomin Abuja sun fara yajin aiki

Kungiyar ƙwadago ta NLC reshen birnin tarayya Abuja ta umarci ma’aikatan dake kananan hukumomin 6 da su fara yajin aiki tun daga ranar 1 ga watan Disamba.

Knabanyi Adalo shugaban kungiyar shi ne ya bada umarnin a wata sanarwa da ya fitar.

Adalo ya ce  an bada umarnin fara yajin aikin ne domin bin matakin sanarwar bayan taron da aka fitar a taron da shugabancin kungiyar NLC na ƙasa ya gudanar a Fatakwal ranar 8 ga watan Nuwamba.

Shugabancin kungiyar ya roki shugabannin ƙananan hukumomin da su fara aiwatar da fara biyan ₦70,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi.

Adalo ya ce shugabannin ƙananan hukumomin sun gaza amsa buƙatar da aka gabatar musu ta aiwatar da fara biyan mafi ƙarancin albashin.

More from this stream

Recomended