Ma’aikata sun maka Unilever a kotu

Unilever ya ce ya na bai wa ma'aikatansa duk wani taimako da suke bukata


Unilever ya ce ya na bai wa ma’aikatansa duk wani taimako da suke bukata

Wasu ma’aikata su 10 a Kenya sun shigar da karar kamfanin Unilever na Burtaniya da Holland a gaban kotun koli da ke London, akan gaza daukan nauyin da ya rataya a wuyansa na kare hakkin dan adam a rikicin bayan zaben shekara ta 2007.

Ma’aikatan sun ce kamfanin ya nuna halin ko-in-kulla wajen kare rayukansu a lokacin, zargin da Unilever ya musanta.

Sama da mutum dubu 1 aka kashe a rikicin.

A lokacin shigar da karar ma’aikatan sun ce akwai masu yiwa kamfanin aiki su 7 cikin wadanda aka kashe, sannan an aikata fyade akan mata 56.

Wakilin BBC ya ce ma’aikatan sun ce shugabanin gudanarwar kamfanin a Kenya sun jefa rayuwarsu a cikin hatsarin barazanar mutuwar bayan ma’aikatan sun shigar da korafinsu.

Sai dai Unilever ya ce ya bai wa ma’aikatansa duk wani taimako da suke bukata a wannan lokaci.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...