Ma’aikaciyar Banki Za Ta Shafe Shekaru Biyar A Gidan Yari A Kan Damfara Ta N22m A Kano

Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Ƙasa, EFCC, ta samu nasarar gurfanar da wata ma’aikaciyar banki, Janet Theophilus Danjuma, kan damfarar wani mai zuba jari kuɗi har N22,350,000 ta hanyar wata zamba ta jari da ba ta wanzu ba a Kano.

An yanke mata hukuncin ne a ranar Litinin, 16 ga Fabrairu, 2026, a gaban Mai Shari’a S. M. Shuaibu na Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Kano. Kotun ta tura ta gidan yari na tsawon shekaru biyar ba tare da zaɓin biyan tara ba.

Danjuma, wadda ma’aikaciya ce a Taj Bank Limited, reshen Nai’bawa, an gurfanar da ita ne kan tuhuma guda ɗaya da ta shafi karɓar kuɗi ta hanyar yaudara.

A cewar takardar tuhuma, laifin ya faru ne a watan Oktoban 2024 a Kano, inda ta karɓi kuɗin daga hannun Wade Bamaiyi da sunan cewa za ta saka su a cikin shirin ajiyar bankin na CASA (Current Account Savings Account).

Tuhumar ta ce: “Janet Theophilus Danjuma, being a staff of Taj Bank Limited, Nai’bawa Branch Kano, sometime in October 2024 in Kano, within the jurisdiction of this Honourable Court, with intent to defraud, did obtain the sum of N22,350,000 from Wade Bamaiyi under the pretext that the money would be invested in CASA Programme of Taj Bank Limited, which pretext you knew to be false and thereby committed an offence contrary to Section 1(1)(b) and punishable under Section 1(3) of the Advance Fee Fraud and Other Fraud Related Offences Act, 2006.”

Ta amsa laifin da ake tuhumarta da shi lokacin da aka karanta mata ƙarar a gaban kotu.

Lauyan masu gabatar da ƙara, Sadiq Huseini, ya bayyana wa kotu yadda wadda ake ƙara ta yi amfani da matsayinta na ma’aikaciyar banki domin samun amincewar wanda aka damfara.

More from this stream

Recomended