Lionel Messi: Barcelona ta rantse ba za ta sayar da ɗan wasan ba, Koeman na son Wijnaldum

Lionel Messi

Mahaifin Lionel Messi da wakilinsa, Jorge, sun gana da shugaban Barcelona Josep Maria Bartomeu, wanda ya shaida musu cewa ba zai sayar da dan wasan Argentina, mai shekara 33 ba. (Marca)

Ganawar farko da aka yi tun bayan Messi ya nemi barin Barcelona ta tashi baram-baram, inda kungiyar ta ce dole ya kammala kwangilarsa ta shekara biyu. (Mundo Deportivo – in Spanish)

Kundin da Barcelona za ta karba idan Messi zai bar kungiyar zai iya zama kasa da euro 100 m (£88.8m), in ji jaridar Telegraph.

An gayyaci Manchester United ta sasanta da Bayern Munich kan dan wasan Sufaniya Thiago Alcantara, mai shekara 29. (ESPN)

Sabon kocin Barcelona Ronald Koeman yana so kungiyar ta yi duk abin da za ta iya domin dauko dan wasan Liverpool da Netherlands Georginio Wijnaldum, mai shekara 29. (ESPN)

Aston Villa na fuskantar gogayya daga wurin Newcastle kan dan wasan Bournemouth da Ingila Callum Wilson, mai shekara 28. (Telegraph)

Paris St-Germain ta yi watsi da damar dauko dan wasan Faransa mai shekara 21 Matteo Guendouzi daga Arsenal. (Telegraph)

DC United ta nemi dauko dan wasan Juventus Gonzalo Higuain, mai shekara 32, kuma tana son dauko dan wasan Everton dan kasar Iceland Gylfi Sigurdsson, mai shekara 30. (The Athletic – subscription required)

Kasashen Faransa da Ingila da Sufaniya da kuma China suna son dauko dan wasan Argentina Higuain, a cewar wakilinsa. (Tuttosport – in Italian)

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...