Lionel Messi: Barcelona ta rantse ba za ta sayar da ɗan wasan ba, Koeman na son Wijnaldum

Lionel Messi

Mahaifin Lionel Messi da wakilinsa, Jorge, sun gana da shugaban Barcelona Josep Maria Bartomeu, wanda ya shaida musu cewa ba zai sayar da dan wasan Argentina, mai shekara 33 ba. (Marca)

Ganawar farko da aka yi tun bayan Messi ya nemi barin Barcelona ta tashi baram-baram, inda kungiyar ta ce dole ya kammala kwangilarsa ta shekara biyu. (Mundo Deportivo – in Spanish)

Kundin da Barcelona za ta karba idan Messi zai bar kungiyar zai iya zama kasa da euro 100 m (£88.8m), in ji jaridar Telegraph.

An gayyaci Manchester United ta sasanta da Bayern Munich kan dan wasan Sufaniya Thiago Alcantara, mai shekara 29. (ESPN)

Sabon kocin Barcelona Ronald Koeman yana so kungiyar ta yi duk abin da za ta iya domin dauko dan wasan Liverpool da Netherlands Georginio Wijnaldum, mai shekara 29. (ESPN)

Aston Villa na fuskantar gogayya daga wurin Newcastle kan dan wasan Bournemouth da Ingila Callum Wilson, mai shekara 28. (Telegraph)

Paris St-Germain ta yi watsi da damar dauko dan wasan Faransa mai shekara 21 Matteo Guendouzi daga Arsenal. (Telegraph)

DC United ta nemi dauko dan wasan Juventus Gonzalo Higuain, mai shekara 32, kuma tana son dauko dan wasan Everton dan kasar Iceland Gylfi Sigurdsson, mai shekara 30. (The Athletic – subscription required)

Kasashen Faransa da Ingila da Sufaniya da kuma China suna son dauko dan wasan Argentina Higuain, a cewar wakilinsa. (Tuttosport – in Italian)

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...