Likitar Najeriya ta yi nasarar samun damar ci-gaba da aiki a Ingila

[ad_1]

Dr Hadiza Bawa-Garba

Hakkin mallakar hoto
PA

Image caption

An sami likita Hadiza Bawa-Garba da laifin kisan kai bisa kuskure ta hnayar tsantsan sakaci a shekarar 2015

Wata likita wadda aka fitar da sunanta daga jerin sunayen likitoci saboda mutuwar wani yaro mai shekara shida ta yi nasara a daukaka karar da ta yi ta neman damar ci-gaba da aikin likita.

An cire sunanta ne a watan Janairun shekarar 2018.

Daukaka kararta ta sami tallafin ma’aikatan kiwon lafiya domin sun ce hukuncin zai rage wa ma’aikatan kiwon lafiya kwarin gwiwar bayyana gaskiya a lokacin da ake bincike kan kurakurai.

Hukuncin ya biyo bayan Jack Adcock mai shekara shida wanda ya mutu a asibitin Leicester Royal Infirmary a shekarar 2011 a lokacin da wata cuta mai suna sepsis wadda ba a gano ba ta janyo masa bugun zuciya.

Kare alumma

An dakatar da likita Bawa-Garba daga jerijn sunayen likitoci masu aiki na shekara daya a watan Yunin shekarar 2017.

Duk da haka, hukumar kula da aikin kiwon lafiya a Ingila (GMC) ta daukaka kara kan hukuncin tana mai ikirarin cewar bai “kai ya kare dukkan mutane ba” kuma an cire sunanta daga sunayen likitoci a watan Janairun 2018.

Dubban likitoci sun rattaba hannu kan wata budaddiyar wasikar goyon bayan likita Bawa-Garba, suna masu cewar shari’ar za ta “rage damammakinmu na hana aukuwar irin mutuwar”.

Daga farko dai, manyan alkalai uku sun soke hukuncin babbar kotun kuma suka tabbatar da karamar ladabtarwar dakatarwar shekara daya.

Alkalin kotun daukaka kara, Sir Terence Etherton, wanda ya bayyana hukuncin, ya ce “ba a taba nuna wata fargaba” ba “game da kwarewar Dr Bawa-Garba a aikin likita, fiye da mutuwar Jack”.

Hakkin mallakar hoto
Adcock family

Image caption

Jack died at Leicester Royal Infirmary in 2011 when undiagnosed sepsis led to cardiac arrest

Ya ce “Hujjara da ke gaban kotu ta nuna cewa tana kashi daya cikin uku na awadanda suka fi hazaka cikin wadanda suke karatun kwarewa tare.”

Ababen damuwa’

Charlie Massey, shugaban hukumar GMC, ya yarda da hukuncin kotun daukaka karar.

Ya ce: “A matsayinmu na hukumar dake kare marasa lafiya ana yawan kiranmu mu dauki matakai masu wuya, kuma ba ma wasa da wannan aikin.”

Mista Massey ya kara da cewa lamarin ya “fitar da ababen damuwa” dangane da hurumin dokokin laifuka a harkar kiwon lafiya kuma hukumar GMC ta bayar da aikin bincike mai zaman kansa sakamakon wannan lamarin.

“Likitoci sun kalubalance mu mu fito domin kare wadanda ke aiki a cikin yanayi mai wuya, kuma wannan ne muke kara matsa kaimi wajen yi,” in ji shi.

Hakkin mallakar hoto
PA

Image caption

An cire sunan Dr Hadiza Bawa-Garba (dake dama) bayan hukumar dake sa ido akan aikin likitoci ta daukaka kara

[ad_2]

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...