Labarin ɓacewar al’aura ƙarya ne—Ƴan sanda

‘Yan sanda a Borno a ranar Talata sun yi watsi da rahoton bacewar al’aurar maza a Maiduguri.

Mai magana da yawun ‘yan sandan, ASP Nahum Daso, ya bayyana ikirarin da wasu suka yi a matsayin labari mara tushe.

Mista Daso ya bayyana cewa ‘yan sanda sun samu bayanan karya da wasu mutane ke yadawa kan bacewar al’aurarsu yawanci bayan sun yi musabaha da baƙi.

Ya kara da cewa wadanda abin ya shafa da suka kai kara an kai su asibiti domin duba lafiyarsu sai dai an gano cewa zargin ba shi da tushe balle makama domin al’aurarsu na nan daram kuma tana aiki.

“Akan haka ‘yan sanda na son sanar da mutanen Borno kada su firgita; su kasance masu bin doka da oda tare da yin watsi da bayanan da ba su dace ba da ke iya haifar da rashin jituwa da rushe yanayin zaman lafiya a jihar.

More from this stream

Recomended