[ad_1]
Wasu daga cikin hotunan abubuwan da suka faru a Afrika a makon jiya .
Hakkin mallakar hoto
AFP
Clare Byarugaba, jaridar kasar Uganda, ta bayanna a matsayin ‘yar madugo a wajen wasannin ‘yan luwadi da aka yi a Paris a ranar Juma’a
Hakkin mallakar hoto
AFP
… ” Ina alfahari da wakilatar kasata a wasannin. Sai dai na san zan fuskanci matsala idan na koma gida”, in ji ta.
Hakkin mallakar hoto
AFP
Wasun masu wasan gargajiya daga kasar Thailand a wasan raya aldaun gargajiya da aka yi a Tunisia.
Hakkin mallakar hoto
Getty Images
Wata kirista mabiyar darikar kataloka daga Zambia na tafiya a filin da aka yi aka baje kolin talkalma a wajen cocin Westminster da ke Landan a ranar Laraba. Shirin na goyon bayan fafutukar da Fafaroma Francis yake yi kan ‘yan gudun hijira
Hakkin mallakar hoto
AFP
Wata ‘yar wasan kwallon kafar Ghana ta shuri mai tsaron gidar New Zealand da kafa a gasar kwallon kafa ta mata masu shekaru kasa da 20 da ake yi a Faransa.
Hakkin mallakar hoto
AFP
Lazarus Molatlhegi na kallon hoton mahifinsa, Thomas Molatlhegi, daya daga masu fafutukar ‘yantar da nahiyar Afrika da aka kashe ta hanyar ratayewa a 1964, kan kisan da aka yi wa wani dan sanda a Afrika ta kudu. An sake fitar da gawarsa domin iyalinsa su yi masa jana’iza yadda ya kamata.
Hakkin mallakar hoto
AFP
Wasu mata a Jamhuriyar Beni na zaman makoki kan mutuwar sarkin Dah Dedjalagni Agoli-Agbo, na masauratarr Dahomey.
Hakkin mallakar hoto
AFP
Wata jami’ar hukumar zabe a Mali na nuna yadda za a kada kuria a ranar Lahadi. Shugaba Ibrahim Boubacar Keïta ya doke abokin hammyarsa Soumaïla Cissé a zaben zagaye na biyu, wanda ‘yan adawa suka ce an yi magudi.
Hakkin mallakar hoto
AFP
Gangamin yakin neman zabe da aka yi Bamako babban birnin kasar Mali
Hakkin mallakar hoto
AFP
Wani yaro a kasuwar sayar da shanu da ke Masarya yayin da aka soma shirye-shiryen bukukuwan Sallar layya.
Hotuna daga AFP da Getty Images
[ad_2]