A cigaba da neman amincewar ya’yan jam’iyar PDP su sahale masa ya zama ɗan takarar shugaban kasa, a tutar jam’iyyar, tsohon gwamnan Kano , Rabi’u Musa Kwankwaso ya ziyarci jihar Niger.
Rahotanni sun nuna cewa tsohon gwamnan ya samu kyakkyawar tarba daga dubban magoya bayansa.
A jawabinsa ga yan jam’iyar ta PDP, Kwankwaso ya yi kira ga sauran yan takara da su hada kai domin tunkarar shugaban kasa Muhammad Buhari.
Kwankwaso ya ce ya fita daga jam’iyar APC ne bayan ya ga canjin da aka samu ba irinsa suka yi wa mutane alkawari ba lokacin da suke neman mulki a shekarar 2015.