[ad_1]
A cigaba da ziyarar tattaunawa da yake da jagororin jam’iyar PDP na kasa baki da daya, tsohon gwamnan jihar Kano kuma sanata a yanzu dake wakiltar mazabar Kano ta tsakiya a majalisar dattawa, Rabiu Musa Kwankwaso ya ziyarci Jihar Rivers.
Kwankwaso ya gana da gwamnan jihar,Barrister Nyesom Wike gwamnan da ake gani na daga cikin gwamnonin da suke fada aji cikin jam’iyar PDP.
Sanata Kwankwaso na daga cikin yan takara dake neman jam’iyar PDP ta tsayar takarar shugaban a zaɓen shekarar 2019.
Bayan ganawar da ya yi da Wike Kwankwaso ya kuma tattauna da shugabannin jam’iyar ta PDP na jihar.
Rahotanni sun nuna cewa Kwankwaso ya samu kyakkyawar tarba daga magoya bayansa.
[ad_2]