Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam’iyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a jihar Borno ta shafa.

Kwankwaso ya sanar da bayar da tallafin ne a lokacin da ya kewa gwamnan jihar Babagana Umara Zulum jajen ambaliyar ruwan da ta shafi wani sashe na birnin Maiduguri.

Tsohon gwamnan ya jajantawa al’ummar jihar inda ya bayyana alhininsa  tare da miƙa saƙon ta’aziyarsa kan mutanen da suka mutu a ambaliyar ruwan.

Da yake ƙarbar tallafin kuɗin a fadar gwamnatin jihar Borno, gwamna Zulum ya godewa Kwankwaso inda ya yi addu’ar Allah ya cigaba da ƙara masa lafiya da yalwar arziki.

A lokacin ziyarar jajen Kwankwaso  na tare da shugaban jam’iyar NNPP na ƙasa, Dr. Ahmad Ajuji, Engr Buba Galadima, Hon Abba Kawu Ali, Dr Umar Alkali da kuma ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Tarauni, Mukhtar Umar Yarima.

More News

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...