Kungiyar Myetti Allah Tace Bata Shiga Harkokin Siyasar Najeriya

[ad_1]

Sakataren kungiyar na Kasa, Baba Usman Ngelzarma ya shaidawa sashen Hausa na Muryar Amurka cewa sun sami labarin cikin kaduwa, kuma tuni suka kaddamar da bincike akan maganar, da wani mai suna Garus Gololo ya yi da sunansu, yace muddin suka tabbatar da hakan to zasu dauki mataki akansa.

Baba Usman Ngelzarma ya nesanta kungiyar Myetti Allah da shiga harkar siyasa ta kowacce siga, kana yace, Garus Gololo da aka ce ya bada wa’adin a madadin Myetti Allah, shi ba kowa bane a kungiyar don haka ba shi da hurumin Magana da yawunsu.

Babban sakataren Myetti Allah ya ce an kafa kungiyarsu ne da zummar kare muradin Fulani makiyaya, kuma ba ruwan kungiyar da duk wata harkar siyasa.

A nasa bangaren, Garus Gololo da aka ce ya fidda sanarwar, ya ce shi babban jami’i ne a kungiyar Myetti Allah ta kasa, amma ba da yawun kungiyar ya bada sanarwar ba. Ya kuma shaidawa muryar Amurka cewa ya bada sanarwar ne a madadin sa na Uban kungiyar Fulani Yan Jam’iyyar APC na Najeriya.

Gololo ya kara da cewa, a matsayinsa na dan jam’iyyar APC yana da ‘yancin fadin albarkacin bakinsa duba da yadda Bukola Saraki ya fice daga Jam’iyyar, don haka ya kamata ya sauka daga kujerarsa don wani dan APC ya maye gurbinsa.

Garus Gololo ya zargi Bukola Saraki da jan kafa wajen tabbatar da majalisar ta yi aiki akan kasafin kudi da ma wasu hidindimu da suka shafi kasa da ci gabanta.

Saurari rahoton Hassan Maina Kaina

[ad_2]

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...