Kungiyar ƙwadago ta NLC ta gudanar da zanga-zanga a faɗin Najeriya

Mambobin kungiyar kwadago ta NLC sun fara gudanar da zanga-zangar lumana domin nuna adawarsu da cire tallafin man fetur.

A jihar Lagos masu zanga-zangar sun taru a karkashin gadar Ikeja inda suka fara zanga-zangar.

A can birnin tarayya Abuja an samu rahoton karya kofar shiga harabar majalisar tarayya a lokacin da aka yi kokarin hana yan kungiyar ta NLC shiga ciki.

A makon da ya gabata ne kungiyar ta NLC ta bawa gwamnatin tarayya wa’adin mako daƴa domin ta janye duk wasu tsare-tsarenta da ke musgunawa talaka.

Zanga-zangar dai ta gudana lafiya a jihohi da ke fadin Najeriya.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...