Kungiyar ƙwadago ta NLC ta dage kan tsunduma yajin aiki

Kungiyar ƙwadago ta NLC ta ce babu wata yarjejeniya da ta shiga da gwamnatin tarayya domin ta dakatar da shiga yajin aikin sai baba ta gani da kuma zanga-zanga da ta shirya farawa a ranar 3 ga watan Oktoba.

A ranar Laraba, Olajide Oshundun daraktan yaÉ—a labarai na ma’aikatar Æ™wadago da ayyukan yi aka jiyo shi yana fadin cewa an cimma matsaya tsakanin gwamnatin tarayya da kuma kungiyar NLC kan janye kudirin shiga yajin aikin.

A yayin da Oshundun ya musalta faÉ—in wannan maganar shima sashen yaÉ—a labarai da hulda da jama’a na kungiyar NLC ya musalta rahoton a cikin sanarwar da ya fitar ranar Alhamis.

Shugaban sashen Benson Upah shi ne ya bayyana haka a cikin sanarwar.

“Bamu da wata yarjejeniya da gwamnati kan janye yajin aikin da aka shirya ko. Ba mu da kuma wata rana da aka saka ta yin taro da gwamnatin tarayya da zai kai ga an janye yajin aikin da aka shirya shiga.” ya ce

More News

An sake gano gawar wani shugaban Fulani da ya ɓata a jihar Filato

An gano gawar wani Arɗon Fulani, Umar Ibrahim da ya ɓace a cikin wata rijiya dake kauyen Jokom a ƙaramar hukumar Mangu ta...

An kama Æ´an kungiyar IPOB 18 da ake zargi da kisan Æ´an sanda

Rundunar yan sandan jihar Imo ta kama mutane 18 da ake zargi da zama yan kungiyar IPOB da suke da hannu a kisan Æ´an...

Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da zaɓen gwamnan jihar Sokoto

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja ta tabbatar da zaɓen, Ahmed Aliyu a matsayin gwamnan jihar Sokoto. Rukunin alkalan kotun su uku sun yi watsi da...

Kotun ɗaukaka ta soke zaɓen shugaban majalisar dokokin jihar Kaduna

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja, ta soke zaɓen kakakin majalisar dokokin jihar Kaduna, Yusuf Liman. Alkalan kotun uku sun bayar da umarni da a sake...