Ku san Malamanku: Sheikh Sharif Ibrahim Saleh

Bayanan bidiyo,
Ku san Malamanku: Sheikh Sharif Ibrahim Saleh

Fitaccen malamin addinin Musuluncin nan a Najeriya, Sheik Sharif Ibrahim Saleh ya ce ya rubuta litattafai fiye da 400 na addinin Musulunci da hannunsa.

Malamin, wanda jigo ne a ɗariƙar Tijjaniya a ƙasar ya faɗi hakan ne a wata hira da ya yi da BBC Hausa a sabon shirinmu na musamman mai taken ”Ku San Malamanku”.

Wannan shiri zai dinga kawo muku hira ta musamman ne kan abubuwan da suka shafi rayuwar manyan malaman addinin Musulunci har ma da na Kirista, don sanin abubuwan da suka shafe su.

Shirin ya fara ne da Sheik Sharif Ibrahim Saleh, wanda ya yi karatu a wurare da dama da suka haɗa da Makka da Madina da Masar da Pakistan da sauran su, a wajen manyan malaman Musulunci, ciki har da babban makarancin Ƙur’anin nan Mahmud Khalilul Khusari a Masar.

Sheikh Shariff Saleh shi ne shugaban kwamitin fatawa ta addinin musulunci a Najeriya.

Sheik Sharif ya ce ya fi sha’awar ɓangaren ilimin Ƙur’ani da Hadisi kuma a nan ne ya fi ƙwarewa. Sannan ya haddace Hadisan da suke cikin Bukhari da Muslim da sauran manyan litattafan hadisai.

Malamin dai ɗan ƙabilar Shuwa Arab ne, sannan ya ce ya fi son abinci mara yaji.

A cikin hirar, Sheikh ya ce ya kamata malamai su daina hauragiya da zage-zagen juna. “Kamata ya yi su haɗa kai wajen ilimantar da mutane.”

Sannan ya koka kan yadda ya ce ake siyasa a Najeriya ba don ci gaban al’umma ba.

Wane ne Sheik Sharif Ibrahim Saleh?

An haifi Sheikh Sharif Ibrahim Saleh a ranar Asabar, 12 ga watan Mayun 1938 a garin Aredibe, da ke kusa da Dikwa ta Jihar Borno.

Mahaifinsa, shi ne Sheik Muhammad Al-Salih bin Yunus Al-Nawwy, wanda wani babban malami ne da ya yi fice a fagen ilimin addinin Musulunci.

Sheik Ibrahim Saleh ya fara koyon Al-Ƙur’ani mai girma tun yana ɗan ƙaramin yaro, inda a kullum yake tare da mahaifinsa da dare wanda kullum aikinsa shi ne yin nafila cikin dare.

Wannan ne ya sa Malamin ya fara haddace ayoyin Ƙur’ani tun kafin ya shiga makaranta gadan-gadan. Sau da dama ɗaliban da ke karatu a wurin mahaifinsa na yawan mamakin Ibrahim kan irin ƙoƙarinsa da basirarsa sakamakon yadda yake cin su gyara a karatu duk da sun sha gabansa.

Daga shekarun 1944 zuwa 1964 ne malamin ya matsa ƙaimi wajen haddace Ƙur’ani da koyon wasu litattafai da darusa.

Ya kuma fara neman ilimin Ƙur’ani ne tun a cikin gidansu, wanda daga baya ya koma sauran tsangayu inda ya je wurare kamar Tarmuwa da Gulumba da Gide da Maishumari da Maiduguri.

Akwai manyan malamai da dama da suka yaba da ƙoƙarin Sheik Ibrahim Saleh tun yana ƙarami kamar irin su Sheik Ahmad Muhammadul Habib, wanda jika ne ga Sheik Al-Tijani, akwai kuma Sheik Muhammad Mustapha Alawi da Sheik Tijjani Usman da dai sauransu.

Sheik Ibrahim Saleh ya shafe shekara 20 yana neman ilimi a matsayinsa na ɗalibi, kuma ya koyi kusan dukkan karatunsa a Najeriya, amma ba hakan ke nufin duka malamansa ƴan Najeriya ba ne.

Karatun Sheik Ibrahim ya fi ƙarfi a ɓangaren Hadisi da Usulul Fiƙihu da Ilmun Kalam da kuma Tafisiri. Misali, duk wata aya daga cikin Ƙur’ani idan aka ambato ta, malamin zai iya faɗin idan tana da alaƙa da wani hadisi a tattare da ita. Malamin ya kuma yi nisa ƙwarai a karatun Tauhidi da Fiƙihu.

Sheik Ibrahim ya yi aiki da gwamnatoci daban-daban tun daga 1976 musamman gwamnatin tarayya.

Mai ba da shawara

Ana yawan saka shi a duk wani kwamitin addinin Musulunci da zai bayar da shawara kan wasu tsare-tsare da gwamnati ke son ɓullowa da su da ke suke da muhimmanci ga addini ko kuma waɗanda za su iya jawo matsala.

Ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda gwamnatin ƙasar ke yawan tura wa zuwa ƙasashe a matsayin wakilan gwamnati ko kuma cikin wata tawaga zuwa ƙasashe kamar Saudiyya da Iran da Masar da Turkiyya da Libiya da Moroko da dai sauransu.

Sheik Ibrahim Saleh ya rubuta sama da litattafai 400 ya kuma gabatar da ƙasidu sama da 100 duka a harshen Larabci.

Wasu karin labaran da zaku so karantawa

(BBC Hausa)

More from this stream

Recomended