Kotun koli ta dage sauraron karar shari’ar sauya kuÉ—in Naira

Kotun Koli ta dage sauraron karar da wasu Gwamnoni suka shigar kan canjin kudin da Babban Bankin Najeriya (CBN) ya yi zuwa ranar Laraba mai zuwa.

Gwamnonin Jihohin Kaduna da Kogi da Zamfara ne dai suka garzaya kotun suna neman a hana Babban Bankin Najeriya CBN daina amfani da tsoffin takardun kudi na N1,000 da N500 da kuma N200 daga ranar 10 ga watan Fabrairun 2023.

Kotun dai, a yayin zamanta na ranar Laraba ta dage ci gaba sauraron karar har zuwa ranar Laraba, 22 ga watan Fabrairun 2023.

A yayin zaman kotun na yau an samu karin wasu jihohi da suka nemi a saka su a cikin jerin waÉ—anda suke kara da kuma wasu jihohin dake neman a saka su bangaren waÉ—anda ake kara.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...