Kotun ɗaukaka ta soke zaɓen shugaban majalisar dokokin jihar Kaduna

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja, ta soke zaɓen kakakin majalisar dokokin jihar Kaduna, Yusuf Liman.

Alkalan kotun uku sun bayar da umarni da a sake zaɓe a wasu akwatuna biyar.

A watan Satumba, kotun sauraren kararrakin zaɓe dake Kaduna ta kori Liman inda ta bada umarnin sake a zaɓe a wasu akwatuna 42.

Ɗan takarar jam’iyar PDP, Solomon Katuka shi ne ya shigar da ƙara a gaban kotun kan zaɓen na Mazabar Makera.

Rashin gamsuwa da hukuncin ya saka Liman wanda shi ne ɗan takarar jam’iyar APC ya ɗaukaka ƙara.

Kotun ɗaukaka ƙarar ta kori ƙarar da ya ɗaukaka inda ta bayar da umarnin sake zaɓen a akwatuna biyar.

Kotun ta yanke hukuncin cewa tazarar kuri’u 382 tsakanin Liman da Katuka ba su kai yawan katin zaɓen da aka karba a akwatunan ba.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...