Kotun ɗaukaka ta soke zaɓen shugaban majalisar dokokin jihar Kaduna

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja, ta soke zaɓen kakakin majalisar dokokin jihar Kaduna, Yusuf Liman.

Alkalan kotun uku sun bayar da umarni da a sake zaɓe a wasu akwatuna biyar.

A watan Satumba, kotun sauraren kararrakin zaɓe dake Kaduna ta kori Liman inda ta bada umarnin sake a zaɓe a wasu akwatuna 42.

Ɗan takarar jam’iyar PDP, Solomon Katuka shi ne ya shigar da ƙara a gaban kotun kan zaɓen na Mazabar Makera.

Rashin gamsuwa da hukuncin ya saka Liman wanda shi ne ɗan takarar jam’iyar APC ya ɗaukaka ƙara.

Kotun ɗaukaka ƙarar ta kori ƙarar da ya ɗaukaka inda ta bayar da umarnin sake zaɓen a akwatuna biyar.

Kotun ta yanke hukuncin cewa tazarar kuri’u 382 tsakanin Liman da Katuka ba su kai yawan katin zaɓen da aka karba a akwatunan ba.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...