Kotun ɗaukaka ta soke zaɓen shugaban majalisar dokokin jihar Kaduna

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja, ta soke zaɓen kakakin majalisar dokokin jihar Kaduna, Yusuf Liman.

Alkalan kotun uku sun bayar da umarni da a sake zaɓe a wasu akwatuna biyar.

A watan Satumba, kotun sauraren kararrakin zaɓe dake Kaduna ta kori Liman inda ta bada umarnin sake a zaɓe a wasu akwatuna 42.

Ɗan takarar jam’iyar PDP, Solomon Katuka shi ne ya shigar da ƙara a gaban kotun kan zaɓen na Mazabar Makera.

Rashin gamsuwa da hukuncin ya saka Liman wanda shi ne ɗan takarar jam’iyar APC ya ɗaukaka ƙara.

Kotun ɗaukaka ƙarar ta kori ƙarar da ya ɗaukaka inda ta bayar da umarnin sake zaɓen a akwatuna biyar.

Kotun ta yanke hukuncin cewa tazarar kuri’u 382 tsakanin Liman da Katuka ba su kai yawan katin zaɓen da aka karba a akwatunan ba.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...