Kotun ɗaukaka kara ta tabbatar da zaɓen gwamnan jihar Gombe

Kotun daukaka kara dake zamanta a Abuja ta tabbatar da zaɓen Muhammadu Inuwa Yahaya a matsayin gwamnan jihar Gombe.

Kotun mai alkalai uku dukkansu sun amince cewa jam’iyar PDP da kuma ADC dukkansu sun gaza tabbatar da zargin da suke cewa an saba ka’ida da kuma rashin bin dokokin zaɓe a karar da suka shigar daban-daban a gaban kotun.

Mai shari’a, Orji Abadua wanda ya shine ya karanta hukuncin alkalan ya tabbatar ds hukuncin da kotun sauraren kararrakin zaɓen gwamna ta yi na korar karar da ɗan takarar jam’iyar PDP Jibrin Barde ya shigar.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...