Kotun ɗaukaka kara ta tabbatar da zaɓen gwamnan jihar Gombe

Kotun daukaka kara dake zamanta a Abuja ta tabbatar da zaɓen Muhammadu Inuwa Yahaya a matsayin gwamnan jihar Gombe.

Kotun mai alkalai uku dukkansu sun amince cewa jam’iyar PDP da kuma ADC dukkansu sun gaza tabbatar da zargin da suke cewa an saba ka’ida da kuma rashin bin dokokin zaɓe a karar da suka shigar daban-daban a gaban kotun.

Mai shari’a, Orji Abadua wanda ya shine ya karanta hukuncin alkalan ya tabbatar ds hukuncin da kotun sauraren kararrakin zaɓen gwamna ta yi na korar karar da ɗan takarar jam’iyar PDP Jibrin Barde ya shigar.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...