
Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja ta tabbatar da zaɓen, Ahmed Aliyu a matsayin gwamnan jihar Sokoto.
Rukunin alkalan kotun su uku sun yi watsi da ɗaukaka ƙarar da jam’iyar PDP da ɗan takararta, Saidu Umar suka yi inda suke ƙalubalantar nasarar da Aliyu ya samu.
Dukkanin alkalan uku sun ce ba su ga dalilan da zai sa su yi gyara ga hukuncin kotun sauraren ƙararrakin zaɓen gwamnan da ya bawa Aliyu nasara ba.
Aliyu da ya yiwa jam’iyar APC takara ya lashe zaɓe da kuri’a 453,661 a yayin da Umar ya samu kuri’a 404, 632.
Amma Umar ya yi zargin cewa gwamnan da mataimakinsa Idris Gobir sun miƙawa hukumar INEC takardun kammala makaranta na jabu domin su samu damar tsayawa takara.
Masu ƙarar sun kuma yi zargin cewa anyi magudi a zaben.
Kotun a hukuncinta na ta tace sun gaza tabbatar da gaskiyar zarge-zarge 6 da suka shigar da kara akansu.