Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da zaɓen gwamnan jihar Sokoto

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja ta tabbatar da zaɓen, Ahmed Aliyu a matsayin gwamnan jihar Sokoto.

Rukunin alkalan kotun su uku sun yi watsi da ɗaukaka ƙarar da jam’iyar PDP da ɗan takararta, Saidu Umar suka yi inda suke ƙalubalantar nasarar da Aliyu ya samu.

Dukkanin alkalan uku sun ce ba su ga dalilan da zai sa su yi gyara ga hukuncin kotun sauraren ƙararrakin zaɓen gwamnan da ya bawa Aliyu nasara ba.

Aliyu da ya yiwa jam’iyar APC takara ya lashe zaɓe da kuri’a 453,661 a yayin da Umar ya samu kuri’a 404, 632.

Amma Umar ya yi zargin cewa gwamnan da mataimakinsa Idris Gobir sun miƙawa hukumar INEC takardun kammala makaranta na jabu domin su samu damar tsayawa takara.

Masu ƙarar sun kuma yi zargin cewa anyi magudi a zaben.

Kotun a hukuncinta na ta tace sun gaza tabbatar da gaskiyar zarge-zarge 6 da suka shigar da kara akansu.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...