Kotu Ta Yi Fatali da Karar Da Dr Mailafiya Ya Shigar

Dr Mailafiya ya garzaya kotu ne domin kalulabantar cancantar hukumar ‘yan sanda bisa gayyatar da tayi masa don binciken wasu kalaman da ya furta yayin hira da wani gidan rediyo a Legas, kan rashin tsaro a kudancin Kaduna.

Mai shari’a Arum Ashoms da ya dauki tsawon lokaci yana karanta bayanai kan hukuncin yace hukumar ‘yan sanda na da hurumin gayyatar kowa don samun bayanai.

A hirarshi da Muryar Amurka, Jagoran lauyoyin dake kare Dr. Obadiah Mailafiya, Barista Yakubu Sale Bawa yace zasu yi nazarin hukuncin kafin daukan mataki.

Barrisater Saleh Bawa yace akwai Dokar da ta bayyana cewa, akwai dukar da ta bayyana cewa duk abinda ya jibinci maganar tsaro na cikin gida, hukumar DSS ce take da hurumin kiran mutum ta yi bincike, kuma sun kira Dr Mailafiya ya yi masu bayani, sai dai yace kotun ta bayyana cewa ‘yan sandan suna neman bayanai ne daga wurin wanda yake karewa domin ya taimakesu su a binciken da suke gudanarwa kan korafin da ya yi, da zai kai ga samun hanyar shawo kan matsalar tsaro da ta addabi kasar.

Lauyan bangaren hukumar ‘yan sandan Najeriya, Barista Michael Mayowa Oladipo yace kotu tayi adalci, kuma hukumcin da ta yanke ya yi daidai saboda ‘yan sanda suna da ‘yancin neman bayanai daga wurin kowa domin tabbatar da tsaron kasa.

Tsohon mataimakin bankin Najeriyan dai ya fara shiga takun saka da jami’an tsaro ne inda aka sha gayyatarsa ya yi bayanai bayan hira da ya yi da wani gidan radiyo inda yace yana da kwararan bayanai kan wadanda suke da hannu a tashe tashen hankali da ake fama da shi a kudancin Kaduna.

More from this stream

Recomended