Kotu ta yanke wa likita hukuncin ɗaurin rai-da-rai saboda laifin fyaɗe

Kotun laifukan lalata da cin zarafin cikin gida a jihar Legas da ke zamanta a Ikeja a ranar Talata ta yanke hukuncin daurin rai-da-rai ga daraktan kula da lafiya na gidauniyar kula da cutar daji, Dakta Olufemi Olaleye, bisa laifin lalata da ‘yar uwar matarsa.

Mai shari’a Rahman Oshodi ya yanke masa hukuncin ne bayan ya same shi da laifin lalata da wata yarinya ‘yar shekara 15.

Alkalin kotun ya ce masu gabatar da kara sun iya tabbatar da karar ba tare da wata shakka ba, kuma dukkan shaidun da ke gaban kotun sun tabbatar.

An gurfanar da Olaleye ne a kan laifuka biyu da suka shafi lalata da kuma cin zarafi ta hanyar lalata da ‘yar uwar matarsa.

More News

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...

Gwamnati za ta fara biyan ma’aikata naira 30,000 mafi ƙarancin albashi a Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya sanar da cewa za su fara aiwatar da tsarin mafi ƙarancin albashi naira 30,000 ga ma'aikatan jihar...

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...