Kotu ta yanke wa dan Boko Haram hukuncin kisa

Wata babbar kotun tarayya dake Abuja ta yanke wa, Auwalu Sama’ila mamba a kungiyar Boko Haram,hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan da ta same shi da aikata laifukan ta’addanci.

Alkalin kotun James Omotosho shi ne ya yanke wa Sama’ila hukuncin kisa bayan da ya amsa aikata  laifuka shida da gwamnatin tarayya ke tuhumarsa da aikatawa

Da yake yanke hukuncin alkalin ya ce wanda ake tuhumar bai nuna nadama ba duk da nauyin laifin da ake tuhumarsa da aikatawa.

“Har sai mutum  ya nuna nadama tare da neman yafiyar Ubangiji sannan zai samu rahama,” a cewar alkalin.

“Mai laifin da yake gabana bai nuna alamar nadama ba duk da munanan ayyukan da ya aikata da rayukan da ya kashe da hannunsa.”

“Allah Ya yi jikansa da rahama,”

Sama’ila ya ya fito ne daga garin Gulak a jihar Adamawa kuma an zarge shi da shiga jerin cikin hare-hare da dama da aka kai a tsakanin shekarar 2012 da 2017.

Tuhume-tuhumen da ake masa sun haÉ—a da zama mamba a kungiyar yan ta’adda da aka haramta, samun horon kan ayyukan ta’addanci da yadda ake amfani da makamai da kuma shiga kai hari kan wasu al’ummomi a jihohin Borno da Adamawa.

An same shi da hannu akai hari a Damboa jihar Borno da kuma Gombi da Hong a jihar Adamawa inda aka kashe fararen hula da dakarun soja.

More from this stream

Recomended