Kotu ta tabbatar da hukuncin kisa kan ɗan ƙasar Denmark da ya kashe matarsa da ƴarsa a Lagos

Kotun ɗaukaka ƙara dake Lagos ta tabbatar da hukuncin kisa akan Peter Nielsen wani ɗan ƙasar Denmark kan kisan matarsa da kuma ƴarsa.

A hukuncin da aka yanke ranar Juma’a kotun ɗaukaka ƙarar tayi watsi da ɗaukaka ƙarar da Nielsen ya yi saboda rashin gamsassun hujjoji.

Kotun ɗaukaka ƙarar ta ce gwamnatin jihar Lagos da ta shigar da ƙarar ta gabatar da ƙwararan hujjoji da suke tabbatar da cewa wanda ake zargin ya aikata laifin na kisan kai.

A ranar 13 ga watan Yuni ne na shekarar 2018 gwamnatin Lagos ta shigar da ƙarar Nielsen gaban babbar kotun jihar inda aka yi masa tuhume-tuhume biyu da suka shafi kisan kai.

Laifin ya saɓa da sashe na 223 na kundin dokar manyan laifuka ta jihar Lagos na shekarar 2015.

Ya kashe matarsa mai suna Zainab wacce aka fi sani da Alizee da kuma ƴarsu mai shekaru 3 a ranar 5 ga watan Afrilu na shekarar 2018 a gidansu dake unguwar Banana Island.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...