Gwamnan Filato Mutfwang ya nufi kotun ƙoli

Gwamnan Jihar Filato Caleb Mutfwang ya nufi kotun koli domin neman hakkinsa bayan kotun daukaka kara ta ƙwace kujerar gwamna daga hannunsa.

Idan ba a manta ba kotun daukaka kara da ke Abuja a ranar Lahadi ne ta kori gwamnan jihar Filato, Mutfwang Manasseh na jam’iyyar PDP.

Ta kuma umarci Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, da ta amince da Nentawe Goshwe na jam’iyyar All Progressives Congress, APC, a matsayin zababben gwamna a zaben gwamnan da aka yi ranar 18 ga watan Maris.

Mai shari’a Elfrieda Williams-Dawodu, wadda ya jagoranci kwamitin mutum uku a lokacin da take yanke hukunci, ya buga misali da sashe na 177 na kundin tsarin mulkin kasar, inda ya ce Manasseh ba dan takara ne da PDP ta dauki nauyinsa ba a lokacin zaben.

More News

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...