Kotu ta samu Maman Boko Haram da aikata zamba

QBabbar kotu dake jihar Borno ta daure, Aisha Wakili wacce aka fi sani da “Maman Boko Haram” har tsawon shekaru biyar bayan da aka same ta da aikata zanba cikin aminci.

Ofishin hukumar EFCC dake yaki da yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati shiyar Borno, ya sake a gurfanar da Wakili tare da wasu mutane biyu Tahiru Daura da Prince Shoyode a cikin watan Satumba shekarar 2020 inda ake musu tuhuma biyu da suka hada da hada baki tare da karbar kudi ta hanyar zanba.

Mutanen uku sun hada baki inda suka damfari Saleh Ahmed Said na kamfanin Shuad General Enterprises bayan da suka saka ya kawo musu wake buhu 3000 da kundinsa ya kai 71,400,000 a madadin kungiyar agaji ta Complete Care and Aid Foundation.

Bayan ya kawo kayan ne sai suka bi biyansa kudinsa hakan yasa ya garzaya gaban hukumar EFCC domin neman mafita.

Mutanen za su shafe shekaru biyar da biyan tarar miliyan 30 idan kuma basu biya to za su kara shafe shekara 10 a gidan yari.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...