Kotu Ta Saka Ranar Fara Sauraron Shari’ar EFCC Da ‘Yan Kasar China Biyu

Hukumar EFCC ta gurfanar da mutanen biyu ‘yan asalin kasar China gaban kotu ne akan zargin aikata laifuka biyu da suka hada da bayar da toshiyar baki ga jami’in gwamnati da kuma hada baki wajen aikata ba daidai ba.

Mutanen biyu da ake zargin aikata laifukan Meng Kun da Xu Koi, sun ‘ki amincewa da aikata laifukan lokacin da Alkali ya tambayesu. Akan haka ne lauyan masu shigar da kara ya bukaci kotun ta saka ranar da za a fara sauraren karar, inda aka saka ranar 15 ga watan Yuni.

Shi kuma lauyan dake kare wadanda ake zargin ya nemi Alkalin kotun ya bayar da belin Meng da Xu, inda Alkalin ya amince da hakan amma sai ranar 18 ga wannan watan za a bayar.

Kamar yadda lauyan hukumar EFCC, Isah Maila Gwani, ya shaidawa Muryar Amurka, tun farko dai an kama wadanda ake zargi ne bisa yunkurin baiwa babban jami’in hukumar EFCC cin hanci na kudi, kan wani bincike da ake yi akansu.

More News

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta ɗaure mutumin sa ya yi sama-da-faɗi da kuɗin marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...