Kotu Ta Saka Ranar Fara Sauraron Shari’ar EFCC Da ‘Yan Kasar China Biyu

Hukumar EFCC ta gurfanar da mutanen biyu ‘yan asalin kasar China gaban kotu ne akan zargin aikata laifuka biyu da suka hada da bayar da toshiyar baki ga jami’in gwamnati da kuma hada baki wajen aikata ba daidai ba.

Mutanen biyu da ake zargin aikata laifukan Meng Kun da Xu Koi, sun ‘ki amincewa da aikata laifukan lokacin da Alkali ya tambayesu. Akan haka ne lauyan masu shigar da kara ya bukaci kotun ta saka ranar da za a fara sauraren karar, inda aka saka ranar 15 ga watan Yuni.

Shi kuma lauyan dake kare wadanda ake zargin ya nemi Alkalin kotun ya bayar da belin Meng da Xu, inda Alkalin ya amince da hakan amma sai ranar 18 ga wannan watan za a bayar.

Kamar yadda lauyan hukumar EFCC, Isah Maila Gwani, ya shaidawa Muryar Amurka, tun farko dai an kama wadanda ake zargi ne bisa yunkurin baiwa babban jami’in hukumar EFCC cin hanci na kudi, kan wani bincike da ake yi akansu.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...