Kotu Ta Hana PDP Cire Shugaban Riƙon Jam’iyar

Wata Babbar Kotun Tarayya dake Abuja ta hana jam’iyar PDP dakatar da Umar Damagum daga matsayinsa na shugaban riƙon jam’iyar.

Mai Shari’a  Peter Lifu shi ne ya bayar da umarnin gaggawar a ranar 3 ga watan Mayu da ya hana jam’iyar zaɓar wani mutum domin ya maye gurbin Damagum har sai an kammala shari’ar da aka shiga gabansa.

Umar El-Gash Maina and Zanna Mustapha Gaddama sune suka shigar da ƙarar mai namba FCH/ABJ/CS/579/2024 a gaban kotun ranar 2 ga watan Mayu.

Waɗanda ake ƙara a shari’ar sun haɗa da kwamitin zartarwar jam’iyar, kwamitin amitattun jam’iyar, shugabannin jam’iyar da kuma hukumar zaɓe ta INEC.

Kotun ta dage sauraron ƙarar ya zuwa ranar 14 ga watan Mayu.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...