Kotu ta halasta shan tabar wiwi a Afirka ta Kudu

afirka ta kudu


Masu fafutukar halasta shan wiwi sun yi ta sowa bayan hukuncin kotun

Babbar kotun Afirka ta Kudu ta halasta wa mutanen da suka balaga amfani da tabar wiwi a wuraren taruwar jama’a.

Masu fafutukar ganin an rika amfani da tabar wiwi a kasar sun yi ta sowa suna masu cewa “mun samu kanmu yanzu” bayan kotu ta yanke hukuncin wanda ba a taba yin irin sa ba.

Dukkan alkalan kotun sun kuma amince mutane su rika noman tabar wiwi domin su rika sha.

Gwamnatin Afirka ta Kudu ta yi adawa da halasta shan wiwi, tana mai cewa shan wiwi yana da “illa” ga lafiyar jama’a.

Har yanzu ba ta yi tsokaci kan wannan hukuncin ba, inda ba za a ja da shi ba.

A watan Afrilu, Zimbabwe ta zama kasa biyu a Afirka, baya ga Lesotho, da ta halasta yin amfani da wiwi a matsayin magani.

Wasu ‘yan kasar Afirka ta kudu uku ne wadanda ake tuhuma bisa amfani da wiwi suka kai kara kotu, suna masu cewa haramta shan wiwin ya tauye hakkinsu na walwala.

Hakkin mallaka:BBC Hausa

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...