
Wata babbar kotun jihar Kano ta dage shari’ar da akewa tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje tare da wasu mutane bakwai kan zargin da ake musu na almundahanar kudaden al’umma.
Kotun ta dake shari’ar ne ya zuwa ranar 15 ga watan Afrilun shekarar 2026.
Ganduje tare da matarsa Hafsat Umar da kuma ɗansa Abdullahi Umar na fuskantar tuhume-tuhume 11 da suka shafi cin hanci da rashawa, da hada baki wajen karkatar da biliyoyin kudaden gwamnati.
Sauran wadanda ake kara sun haɗa da Abubakar Bawuro, Jibrilla Muhammad, Lamash Properties Ltd, Safari Textiles Ltd, da kuma Lasage General Enterprises Ltd.
A cigaba da sauraron shari’ar masu kara sun bukaci a cigaba da shari’ar tare da tunatar da kotun cewa akwai bukatar da suka gabatar gabanta ranar 24 ga watan Nuwamba inda suka nemi a basu damar gabatar da karin hujjoji kan wadanda suke kara.
Amma kuma lauyoyi da dama dake wakiltar mutane daban-daban da ake kara a shari’ar sun nemi cewa kotu ta fara duba bukatun da suka gabatar a baya kafin a cigaba da shari’ar.
A ƙarshe bayan sauraron dukkanin bangarorin mai shari’a, Amina Adamu Aliyu dake jagorantar zaman shari’a ta dage shari’ar ya zuwa ranar 15 ga watan Afrilu domin sauraron dukkanin bukatun da lauyoyin suka gaban kotun.

