Kotu ta bayar da belin tsohon gwamnan Taraba Darius Ishaku kan naira miliyan 150

Babbar kotun tarayya dake zamanta a Maitama a Abuja ta bayar da belin tsohon gwamnan jihar Taraba, Darius Ishaku kan kuÉ—i naira miliyan 150.

A ranar Litinin ne aka gurfanar da Ishaku gaban kotun tare da tsohon babban sakataren hukumar dake kula da ƙananan hukumomi da kuma masarautu ta jihar.

Dukkanin mutanen biyu ana masu tuhume-tuhume 15 da suka haÉ—a da haÉ—a baki wajen aikata zamba da kuma mallakawa kansu dukiyar al’umma.

Sun ƙi yarda sun amsa laifinsu bayan da aka karanta musu tuhume-tuhumen da ake musu.

A yayin zaman kotun na ranar Alhamis lauyoyin waɗanda ake ƙara sun gabatarwa da kotun buƙatar neman beli.

Lauyan hukumar EFCC Rotimi Jacob ya ce ba zai soki buƙatar bayar da belin ba.

Mai shari’a, Sylvanus Orji dake sauraron shari’a ya amince da buÆ™atar belin bisa wasu sharuÉ—a da ya gindaya.

More News

TCN na ci gaba da ƙoƙarin gyaran wutar lantarkin da ta lalace kwana biyu

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Najeriya (TCN) ya sanar da ci gaban da aka samu wajen farfado da rukunin wutar kasa bayan wata tangardar...

Magoya bayan jam’iyyar NNPP sun Æ™ona jar hula

Wasu daga cikin mambobin wani tsagi na jam'iyar NNPP sun barranta kansu da jagoran jam'iyar na ƙasa, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso inda suka riƙa...

PDP ta É—auki hanyar warware rikicin jam’iyyar

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya ce  an kawo karshen rikicin cikin gida da ya dabaibaye jami'yar PDP. Mohammed wanda shi ne shugaban Æ™ungiyar gwamnonin...

Dakarun Najeriya sun cafke wasu Æ´an’aiken Æ´anbindiga a Kaduna

Sojoji sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da kaiwa 'yan bindiga sakonninsu a kasuwar ƙauyen SCC da ke ƙaramar hukumar Kachia a...