Kotu ta bawa gwamnatin tarayya damar ƙwace wasu jiragen ruwa dake satar mai

Kotu ta sahalewa gwamnatin tarayya da ta kwace wasu jiragen ruwa guda biyu da aka samu da ɗaukar ɗanyen man fetur na sata a yankin Niger Delta.

A ranar 20 ga watan Janairu ne aka kama jirgin ruwa ma suna MT Kali a lokacin da yake satar mai a rijiyar mai ta Pennington mallakin kamfanin Shell dake jihar Bayelsa.

Kamfanin Tantita Security Services da gwamnatin tarayya ta ɗauka domin hana satar mai a yankin Niger Delta shi ne ya kama jirgin mai ɗauke da ma’aikata 20.

Har ila yau a cikin watan Faburairu aka kama jirgin ruwa mai suna MT Harbor da kuma Spirit lokacin da yake satar mai a rijiyar mai ta Sengana dake gaɓar ruwan jihar Bayelsa.

Ofishin Babban Sifetan Ƴan Sandan Najeriya,Kayode Egbetokun ne ya shigar da ƙara a gaban kotu.

Mai shari’a,  J.K Omotosho alƙalin babbar kotun tarayya dake Abuja ya bayar da umarni da gwamnatin tarayya ta ƙwace jiragen MT Harbor da Sprit da abun da suke ɗauke da shi na wucin gadi.

Alƙalin ya umarci gwamnatin tarayya da ta dakata  har tsawon makonni shida ko wani zai iya zuwa ya bayyana dalilin da zai sa ba za a ƙwace jiragen ba.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...