Kotu ta bawa gwamnatin tarayya damar ƙwace wasu jiragen ruwa dake satar mai

Kotu ta sahalewa gwamnatin tarayya da ta kwace wasu jiragen ruwa guda biyu da aka samu da ɗaukar ɗanyen man fetur na sata a yankin Niger Delta.

A ranar 20 ga watan Janairu ne aka kama jirgin ruwa ma suna MT Kali a lokacin da yake satar mai a rijiyar mai ta Pennington mallakin kamfanin Shell dake jihar Bayelsa.

Kamfanin Tantita Security Services da gwamnatin tarayya ta ɗauka domin hana satar mai a yankin Niger Delta shi ne ya kama jirgin mai ɗauke da ma’aikata 20.

Har ila yau a cikin watan Faburairu aka kama jirgin ruwa mai suna MT Harbor da kuma Spirit lokacin da yake satar mai a rijiyar mai ta Sengana dake gaɓar ruwan jihar Bayelsa.

Ofishin Babban Sifetan Ƴan Sandan Najeriya,Kayode Egbetokun ne ya shigar da ƙara a gaban kotu.

Mai shari’a,  J.K Omotosho alƙalin babbar kotun tarayya dake Abuja ya bayar da umarni da gwamnatin tarayya ta ƙwace jiragen MT Harbor da Sprit da abun da suke ɗauke da shi na wucin gadi.

Alƙalin ya umarci gwamnatin tarayya da ta dakata  har tsawon makonni shida ko wani zai iya zuwa ya bayyana dalilin da zai sa ba za a ƙwace jiragen ba.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...