Wata babbar kotu dake zamanta Effurun karamar hukumar Uvwie ta jihar Delta ta bayar da belin mutane 69 da ake zargi da hannu a shirya auren jinsi.
Lauyan wadanda ake zargi, Mr Ochikwo Ohimor shi ne ya bayyana haka ga manema labarai da yammacin ranar Talata.
Ya ce an bayar da belin waɗanda ake zargi kan kuɗi N500, 000 da kuma mutane biyu da za su tsayawa kowanennsu.
“Waɗanda za su tsaya musunm dole su kasance suna zaune a yankin Effurun inda aka gurfanar da su a cikin watan Agusta.”
A ranar 27 ga watan Agusta ne yan sanda suka kama mutanen a lokaci da suke tsaka da gudanar da bikin auren jinsi.