Wata kotun majistire dake zamanta a Nomansland jihar Kano ta tura, Abdulmajid Danbilki Kwamanda ya zuwa gidan yari.
Alkalin kotun mai shari’a, Aminu Magashi shi ne ya zartar da hukuncin bayan da aka gurfanar da Kwamanda a gabansa.
Ana zargin sa da aikata laifuka uku ciki har da zargin bata sunan gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje.
A cikin wata hira da yayi a gidan wani rediyo mai zaman kansa Kwamanda ya zargi Ganduje da bai wa shugaban kwamitin riko na jam’iyar APC, Mai Mala Buni kudi domin ya rantsar da Abdullahi Abbas a matsayin shugaban jam’iyar na Kano