Kotu ta ɗaure wasu ƴan damfara a Kano

Wata babbar kotun jihar Kano karkashin mai shari’a Ibrahim Musa Karaye ta yanke wa wasu ‘yan damfara biyu, Benjamin Okechukwu Udeagwu da Benjamin Amos Olamide hukuncin daurin shekaru uku a gidan yari bisa samun su da laifin da suka shafi damfara a yanar gizo.

An daure su ne bayan sun amsa laifuka guda daya da suka shafi zamba a yanar gizo bayan da rundunar shiyyar Kano ta EFCC ta gurfanar da su a gaban kuliya.

Takardar laifin da ake tuhumar Udeagwu cewa ta yi: “Kai, Benjamin Okechukwu Udeagwu a wani lokaci a cikin watan Satumba, 2023 a Kano da ke karkashin hurumin babbar kotun Kano, da niyyar zamba, ya samu dala $50 ta hanyar zamba a matsayin Brad George dan kasar Amurka wanda ke nuna cewa kun san karya ne kuma kuka aikata laifin damfara ta hanyar da ta saɓa wa sashe na 321 na dokar Penal Code”

More News

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...