Ko kunsan wadanda suka sayawa Buhari fom din takara?

NCAN


Tun bayan da, shugaban kasa Muhammad Buhari ya bayyana cewa bashi da kudin sayan fom din takarar shugaban kasa a jam’iyyarsa ta APC

Wasu matasan Najeriya sun saya wa shugaban kasar Muhmmadu Buhari fom din takara a kan Naira miliyan 45.

Matasan na kungiyar Nigeria Ambasadors Consolidation Network sun saya wa shugaban fom din ne jim kadan bayan jam’iyyar APC mai mulkin kasar ta fitar da kudaden da masu neman takara a jam’iyyar za su sayi fom.

Fom din shugaban kasa ne ya fi kowanne tsada, da ake sayar da shi a kan Naira miliyan 45.

To sai dai abin da mutane da dama ke mamaki shi ne yadda matasan suka sami miliyoyin kudin da suka sayawa Buhari fom din, a daidai lokacin da wasu ‘yan uwansu matasa ke korafin cewa kudin da jam’iyyar ta sanya ya yi musu tsada.

Akwai masu ra’ayin cewa matasan na rawa ne da bazar wasu manyan ‘yan siyasa da suka ba su kudin sayen fom din, don a nuna cewa har yanzu Buhari yana da farin jini a wajen matasan kasar.

To sai dai shugaban kungiyar ta Nigeria Ambasadors Consolidation Network Barista Sanusi Musa ya ce ko kadan ba bu wani jami’in gwamnati da ya basu kudi.

“Bari in yi rantsuwa, Wallahi tallahi babu wani jami’in gwamnati da ya ba da ko kwabo a kudin da muka biya,” in ji Sanusi Musa.

Ya kara da cewa, matasan sun kai shekara guda suna tara kudi domin sayawa shugaban fom.

“Mutum daya ne, wani dan kasuwa dan kabilar Ibo kadai ya kawo mana gudunmuwar Naira miliyan biyar, da ya ji abin da muke shirin yi,” in ji shi.

A cewarsa sun gamsu da irin shugabancin Buhari, don haka ne suka yanke hukuncin mara masa baya a zaben da ke tafe.
A zaben shekarar 2015 ma Muhammadu Buhari ya samu gudunmuwa daga ‘yan kasar da dama wajen saya masa fom din takara da kuma kudin yakin neman zabe.

Sai dai wasu suna ganin da wuya a wannan karon ya samu irin wannan gudunmuwar, kasancewar wasu ‘yan kasar sun dawo daga rakiyarsa.

Wannan tunanin da wasu ‘yan kasar ke yi na daga dalilan da Sanusi Musa ya bayyana cewa suka saya wa Buhari fom din, domin nunawa jama’a cewa har yanzu matasa suna goyon bayan Buhari.

A shekara 2014 dai kwamitin yakin neman zaben Shugaba Buhari ya fitar da wani kati wanda jama’a za su iya amfani da shi wajen ba wa Buhari gudunmuwa.

To sai dai babu tabbas ko a wannan karon ma za a yi amfani da wannan hanyar.

Kuma idan ma za a yi din shin jama’a za su bayar da gudunmuwa irin yadda suka bayar a baya?

More News

Ƴan sanda sun kama masu sayen kuri’a a zaben gwamnan Edo

Jami'an rundunar Æ´an sandan Najeriya sun kama wasu mutane 9 da ake zarginsu da sayen kuri'a da kuma mallakar kuri'ar da aka riga aka...

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...