A yayin da al’ummar musulmi ke kammala azumin watan Ramadan, wani abu da ya wajaba musulmi mai hali ya yi shi ne fitar da zakkar fidda-kai.
Ita dai wannan zakka kamar yadda addinin musulunci ya yi tanadi, tana da matukar amfani musamman wajen taimaka wa wadanda ba su da abinda za su sa a baka a lokacin bikin sallah.
ZakkaR fidda kai dai sunnah ce daga cikin sunnonin Manzon Allah SAW.
Ana so ne a fitar da wannan zakkar kai kafin tafiya masallacin idi.
BBC ta tattauna da Sheikh Tukur Almannar, malami a garin Kaduna da ke Najeriya, don jin muhimmancin wannan zakka da ma a kan wadanda ta wajaba.
Karin wasu labaran
Za a daure duk wanda aka kama yana bara a Uganda
Mutane sun mutu bayan sun ci shinkafa a wajen bauta