Ko kun san alfanun bayar da zakkar fidda kai? | BBC Hausa

A yayin da al’ummar musulmi ke kammala azumin watan Ramadan, wani abu da ya wajaba musulmi mai hali ya yi shi ne fitar da zakkar fidda-kai.

Ita dai wannan zakka kamar yadda addinin musulunci ya yi tanadi, tana da matukar amfani musamman wajen taimaka wa wadanda ba su da abinda za su sa a baka a lokacin bikin sallah.

ZakkaR fidda kai dai sunnah ce daga cikin sunnonin Manzon Allah SAW.

Ana so ne a fitar da wannan zakkar kai kafin tafiya masallacin idi.

BBC ta tattauna da Sheikh Tukur Almannar, malami a garin Kaduna da ke Najeriya, don jin muhimmancin wannan zakka da ma a kan wadanda ta wajaba.

Karin wasu labaran

Za a daure duk wanda aka kama yana bara a Uganda

Mutane sun mutu bayan sun ci shinkafa a wajen bauta

More from this stream

Recomended