
Rundunar yan sandan jihar Kano ta ce jami’anta sun kama mutane 41 da ake zargin suna da hannu a kisan, Baba Ali DPO din yan sanda na karamar hukumar Rano a jihar.
An kashe Ali a ranar Lahadi a lokacin da wasu fusatattun matasa suka farma ofishin yan sanda na Rano inda suka kone wani sashe na ofishin tare da wasu motoci biyu.
Sun kai farmakin ne biyo bayan mutuwar wani matashi, Abdullahi Musa wanda yan sanda suka kama da maraicen ranar Lahadi biyo bayan korafin da aka shigar wurin yan sanda cewa yana tukin ganganci.
A lokacin da yake tsare jikin Abdullahi ya yi rauni inda aka garzaya da shi asibitin garin Rano kuma washed gari Allah ya yi masa cikawa.
A wata sanarwa da aka fitar ranar Alhamis mai magana da yawun rundunar, Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce harin wani mummunan farmaki ne kan zaman lafiyar al’umma inda ya ci alwashin cewa za a tabbatar an yi adalci.
A cewar Kiyawa, Ibrahim Adamu Bakori kwamishinan yan sandan jihar ya bawa al’ummar jihar tabbacin cewa rundunar za ta tabbatar an kama tare da hukunta wadanda suke da hannu a kisan.