A ranar Litinin ne ake sa ran bude babban taron koli kan zuba jari tsakanin Birtaniya da nahiyar Afurka. Shugabanin kasashen Afrikar 21 ko wakilansu ne ake sa ran za su halarci taron wanda Firaminista Boris Johnson zai karbi bakuncinsa.
Za a yi wannan taro ne dai kasa da makonni biyu kafin kasar ta fice daga Tarayyar Turai wani abu da zai kawo sauyi ga manufofin cinikayyarta. Masana tattalin arziki sun ce wannan taro ya na da muhimmanci ga Birtaniya da za ta kara fadada harkokin kasuwanci da kasashen duniya.
Farfesa Muhamnmad Muttaqa Usman, masani kan harkokin tattalin arziki a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zaria a Najeriya ya shaidawa BBC cewa ana gudanar da taron a kan gaba ne, idan aka lura da kokarin kasashen Afurka na samar da tasu kungiyar ta Tarayyar Afurka.
”Kasashen Afurka su na neman hada hancin cinikayyarsu ta hanyar amfani da Tarayyar Afurka, wanda zai zo daidai da abin da hadakar ke bukatar ganin an cimma kudurin da suke neman cimma daga nan zuwa shekarar 2063.
Shi daman tattalin arziki ba zai bunkasa ba sai ka na hulda da kasashe da yawa, wani abun dubawa shi ne yanzu China ta na da kyakkyawar alakar kasuwanci da kasashen Afurka wanda ya kai ana ganin tattalin arzikinta ya kai ma’aunin kashi 6 cikin 100 a wannan shekara wanda a baya bai kai haka bunkasa ba.”
Sai dai ana fargabar alakar da ke tsakanin Birtaniya da kasashen Afurka babu wani abin azo a gani da Afurkar ke mora, Farfesa ya ce idan kasashen furka kudu da sahara suka ci gaba da tafiya babu ci gaba, babu wutar lantarki, da ababen more rayuwa da cin hanci da rshawa da ya yi wa wasu daga ciki katutu tabbas Birtaniya ce za ta sha romon wanna alaka ta kasuwanci.
Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya na daga cikin shugabannin kasashen Afurka da ke halartar taron a Birtaniya, a daidai lokacin da gwamnatinsa yakin magance cin hanci da rashawa da masana sukai amanna da cewa ya na yi wa tattalin arzikin kasar zagon kasa.