Kasar Jamus Na Taimakawa Wajen Samar Da Zaman Lafiya a Jihar Filato

[ad_1]

A wani taron ‘karawa juna sani wanda ya hada da shugabannin addinai mata da matasa da makiyaya da kuma manoma daga ‘kananan hukumomi biyar da ake yawan samun tashin hankali da ma ‘yan jarida, domin tattaunawa kan musabbabin tashin rikici da ake samu a yankunan da kuma dabarun magancesu.

Mr Akin Omoware, jami’i ne dake aiki a hukumar inganta rayuwar al’umma ta kasar Jamus dake jihar Filato, ya shaidawa Muryar Amurka cewar manufar taron ita ce su ‘kara kwarin gwiwa wa hukumar sasantawa ta jihar Filato ta hanyar horas da masu ruwa da tsaki dabarun fahintar alamun dake haddasa rikici da hanyoyin magancesu ba tare da an samu tashin hankali ba.

Mr Akin, ya ce ba wanda ke amfana da tashin hankali, ko da ma mutum yana ganin kamar akwai ribar da yake samu a yanzu a rikicin dake aukuwa, tabbas watarana zai yi da na sani, saboda duk abin da mutum ya samu ta hanyar rikici, to kuwa ta hanyar rikicin zai rasa shi, don haka dole mu tabbatar mun sanya tubalin da zai taimaka wajen sasantawa da fahintar juna.

Daraktan labarai na gidan rediyo da talabijin mallakar jihar Pilato, Yakubu Tadi ya ce ‘yan Jarida nada gagarumin gudunmowa a harkar tsaro.

Domin karin bayani saurari rahotan Zainab Babaji.

[ad_2]

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...